Ziyarar Kaburbura

Ziyartar kaburbura - kaburburan Annabi da na Imamai da katange su da kuma yin gine - gine a kansu na daga cikin manyan al'amura da mazhabar Shi'a Imamiyya (Masu bin Imamai 12) ta kebantu da su kuma suna bayar da dukkan abu mai tsada da mai sauki cikin imani da dadin zuciya.
Asalin duk wannan kuma shi ne wasiyyar Imamai da kuma zaburar da mabiyansu da kuma kwadaitar da su a kan irin ladan da take da shi mai yawa a gurin Allah Ta'ala,[1] saboda kasancewarta mafifiyar ayyukan biyayya da ibadu bayan ayyukan ibadu wajibai da kuma cewa wadannan kaburburan na daga cikin mafifitan guraren amsa addu'a da juyawa ga Allah Ta'ala.
Kuma suka sanya ta daga cikin ainihin cika alkawura ga Imamai, domin, "ga kowane Imami akwai alkawarinsa a kan majibintansa da mabiyansa, da kuwa cewa daga mafificin cika alkawari, ziyartar kaburburansu na daga mafi kyawun cikawa, duk wanda ya ziyarce su yana mai kwadayin haka da kuma gaskata abinda suka kwadaitar a kai, to su Imaman nasu za su kasance masu ceto gare su ranar Alkiyama."[2]
A cikin ziyarar kaburbura akwai fa'idoji na addini da zamantakewa da suka sa Imamanmu himmatuwa da ita, domin a halin cewa a lokacin da take kara kulla walaya da soyayya tsakanin Imaman da mabiyansu tana kuma sabunta tuna hadisansu da dabi'unsu da jihadinsu saboda gaskiya kuma tana hado kan musulmi wadanda suke a warwatse ta taro su guri guda, domin su san juna kana kuma ta dasa ruhin jawuwa zuwa ga Allah a cikin zukatansu da yankewa zuwa gare shi, da bin umarce-umarcenSa tana kuma cusa musu hakikanin tauhidi a cikin ma'anonin addu'o'in ziyarorin da ke cike da fasaha wadda aka samo daga Ahlul Bait (A.S.) tare da koya musu tsarkin musulunci da sakon Muhammadu (S.A.W.A) da abinda ya wajaba a kan musulmi na daga matabbatan halayen kwarai, da kankan da kai ga Mai tafi da halittu, da gode wa ni'imominSa, don haka ta wannan bangaren tana amfani ne irin na addu'o'in da aka ruwaito wadanda bayaninsu ya riga ya gabata.
Hatta wadansunsu ma sun tattara ne a kan mafi zurfin addu'o'i da madaukakansu kamar ziyarar "Aminullah" wato "Amintaccen Allah" wadda aka ruwaito daga Imam Zainul Abidina (A.S.) yayin da ya ziyarci kabarin kakansa Amirul Muminin[3](A.S.).
Kamar yadda wadannan ziyarorin da aka ruwaito suke fahimtar da matsayin Imamai (A.S.) da irin sadaukarwarsu a tafarkin taimakon gaskiya da daukaka kalmar addini da dagewarsu a ibadar Allah Ta'ala gashi kuma sun zo da salon larabci zalla, da fasaha madaukakiya, da ma'anoni masu sauki wadanda kowa da kowa yake fahimta, kuma suna kunshe da mafifitan ma'anonin tauhidi kuma mafi zurfi tare kuma da addu'a da yankewa zuwa gare shi Ta'ala.
Alal hakika ita tana daga cikin mafi ingancin laduban addini bayan Alkur'ani mai girma da Nahjul Balagha da kuma addu'o'in da aka ruwaito daga garesu (A.S.) domin a cikinta an kunsa dukkan sanin Imamai (A.S.) a takaice dangane da abinda ya shafi wannan sha'ani na addini da gyaran zuciya.
Sa'an nan kuma a cikin ladubban ziyarar akwai koyarwa da shiryarwar da ke karfafa tabbatar da wadannan ma'anonin addini madaukaka wato irinsu daukaka tsarkin ruhin musulmi, da koya wa ruhinsa tausasawa ga fakiri, da sanya shi tausasawa ga fakiri, da iya zama da jama'a da kyawun hali, da son cudanya da jama'a, domin daga ladubanta akwai abinda ya kamata a aikata kafin a fara shiga cikin gurin makabartar domin ziyartarsa.
Daga nan kuma akwai abinda ya kamata a yi a tsakiyar ziyarar da kuma bayan ziyarar. A nan za mu kawo wasu daga cikin wadannan laduban domin fadakarwa a kan abubuwan da take nufi kamar yadda muka fada:

Daga Ladubbanta akwai:

1- Mai ziyarar ya yi wanka yayin fara ziyararsa ya tsarkaka,[4] fa'idar wannan kuwa kamar yadda muke fahimta a sarari yake, ita ce mutum ya tsarkake jikinsa daga kazanta domin ya kubutar da shi daga cututtuka da kuma domin kada mutane l42 su gundara da warinsa kazalika kuma ya tsarkake kansa daga kazanta.
Ya zo a hadisai cewa mai ziyara ya karanta wannan addu'a idan ya gama wanka domin ya fadakar da shi a kan wadannan manufofi madaukaka ya ce:

Ya Allah Ka sanya mani haske da tsarki gare, da kuma tsari wadatacce daga dukkan cuta da ciwo da kuma dukkan bala'i da musiba kuma Ka tsarkake zuciyata da gabobina da kashina da namana da jinina, da gashina da fatata, da bargona da kashina da kuma abinda kasa ta rage shi daga gare ni, kuma Ka sanya mai shaida gare ni ranar bukatata da fakircina da talaucina."

2- Ya sanya mafi kyawun da mafi tsaftar tufafin da yake da su, domin sanya kyawawa da tsaftatattun tufafi abu ne da mutane ke so wa junansu lokacin bukukuwa, kuma hakan na kusantar da su ga junansu tare da sanya soyayya a tsakaninsu, yana kara sa musu daukaka da jin daukaka a zuciyarsu da jin muhimmancin bukin da suke halarta.
Abu da ya kamata mu jawo hankali gare shi a wannan koyarwa shi ne ba a wajabta cewa dole ne mutum mai ziyara ya sanya mafi kyawun tufafi baki daya ba dungum, a'a sai dai ya sanya mafi kyawun abinda yake da iko a kai domin ba kowa ba ne zai iya yin haka, kuma akwai kuntatawa ga raunana wadda tausayawa ba ta bukatar a yi haka, wannan ladabin dai hakika ya gwama tsakanin abinda ya kamata na ado da kuma mafi kyawun tufafin, da kuma kiyaye yanayin fakiri da kuma mai rauni.
3- Ya sanya abinda ya saukaka gare shi na turare, kuma fa'idarsa tamkar ta sanya sabin kaya ce.
4- Ya yi sadaka da abinda ya saukaka gare shi, kuma fa'idar sadaka a irin wannan al'amari sananniya ce, domin a cikin hakan akwai taimakawa ga gajiyayyu da kuma sanya ruhin tausasawa gare su.
5- Ya tafi yana cikin natsuwa da kwanciyar hankali yana mai takaita ganin idonsa. Abinda ke cikin wannan irin natsuwar da girmama alfarmar wannan gurin da kuma wanda ake ziyarta din da kuma mai da hankali ga Allah Ta'ala da yankewa zuwa gare shi, da kuma abinda ke tare da haka din na nesantar damun mutane da matsa musu a yayin wucewa, da kuma rashin munanawa shashensu daga sashe a bayyane yake a sarari.
6- Ya yi kabbara yana cewa "Allahu Akbar" ya yi ta maimaitawa yadda ya so, kuma mai yiwuwa ne a wasu ziyarorin a kayyade kabbarar zuwa dari. Akwai fa'ida a cikin yin haka wadda ke sanya wa ruhi jin girman Allah Ta'ala, da kuma cewa babu wani abu da ya fi Shi girma, da kuma cewa ziyara ba wata aba ba ce illa ibadar Allah da girmama Shi da daukaka Shi ta hanyar raya alamun Allah da karfafa agginin Shi.
7- Bayan kammala ziyarar kuma ga Annabi ko kuma ga Imamai to sai ya yi salla akalla raka'a biyu nafila kuma domin ibada ga Allah kawai, saboda ya yi godiya a kan muwafakar da Ya yi masa ya kuma bayar da ladanta ga wanda ya kai wa ziyarar.
A cikin addu'ar da aka ruwaito wadda mai ziyarar zai karanta bayan wannan salla akwai abinda zai fahimtar wa mai ziyarar cewa wannan salla dai da duk abinda da ya aikata na Allah ne Shi kadai da kuma cewa shi ba ya bauta wa wani baicin Shi kuma ziyarar ba wata abu ba ce face wani nau'in neman kusanci gare Shi Ta'ala.
"Ya Allah gare Ka na yi Salla, gare Ka na yi ruku'u, gare Ka na yi sujada, Kai kadai ba Ka da abokin tarayya, domin babu salla da ruku'u da sujada sai dai gare Ka, domin Kai hakika ne Allah babu abin bautawa sai Kai. Ya Allah Ka yi dadin tsira ga Muhammaddu da zuriyar Muhammadu, kuma Ka karba mini ziyarata, kuma Ka ba ni abinda na roka, domin Muhammadu da zuriyarsa masu tsarki."
A cikin irin wannan addu'ar akwai wani nau'in ladabi da ke bayyana manufofin Imamai da mabiyansu masu koyi da su a ziyartar kabari ga duk wanda ke son ya san hakika, da kuma irin abinda masu jahilta ke kagawa yayin da suke raya cewa wai ziyartar kaburbura ibada ce gare su da neman kusanci gare su da kuma cewa shirka ce da Allah a ibada.
8- Daga ladubban ziyara akwai cewa:
Mai ziyarar ya lizimci kyanutata abota da duk wanda ya zama tare da shi, da kuma karanta magana, sai dai abinda yake alheri, da yawaita zikirin l43 Allah, da kankan da kai, da yawaita salla, da salati ga Annabi Muahmmadu da Zuriyar Muhammadu kuma ya runtse idandunansa, kuma ya gaggauta zuwa gurin mabukata daga cikin yan'uwansa idan
ya ga abubuwa gare su sun yanke, kuma ya taimaka musu, ya kuma nesanci abinda aka hana, da kuma husuma, da yawaita rantsuwa da jayayyar da ta hada da rantse-rantse.[5]
Sa'an nan kuma alal hakika ziyara ba wata aba ba ce face salati ga Annabi ko kuma ga Imami saboda imani da cewa su "suna raye a gurin ubangijinsu ana arzuta su."[6] Don haka su suna jin magana kuma suna amsawa, kuma ya wadatar ka ce alal misali: "Assalamu Alaika Ya Rasulallah." ("Amince Ya tabbata gare ka Ya Manzon Allah".)
Sai dai kuma abinda ya fi shi ne ka karanta abinda aka ruwaito game da addu'o'in ziyara daga Ahlul Bait, Saboda abinda ke cikinta kamar yadda muka ambata na daga madaukakan manufofi, da kuma fa'idojin addini, da zurfin ma'anarsu da fasaharta da kuma abinda ke cikinta na daga addu'o'i masu zurfi da mutum yake juyawa ga Allah Ta'ala da su.


[1] Littafin Kamiluz Ziyarat hadisan da suka siffanta Ladan Ziyartar Kabarin Manzo (S.A.W.A) da na Imamai (A.S.).
[2]Maganar Imam Ridha (A.S.), Kamiluz-Ziyarat Ibin Kaulawaihi shafi na 122 babi na 44, Ladan wanda ya ziyarci Imam Husain (A.S.); Kafi Juzu'i na 4 shafi na 467 hadisi na 2; Man La Yahduruhul Fakih Juzu'i na 2 shafi na 577 hadisi na 316; Tahzih 6. 78 h.3.
[3]Kamiluz Ziyarat shafi na 39 Babi na 11, ziyarar Kabarin Amirul Muminin.
[4] Kamiluz Ziyarat shafi na 184 Babi na 75 daga cewa wanda ya yi wanka da ruwan Furat ya ziyarci Imam Husain (A.S.) 198 Babi na 79 ziyarar Imam Husain Bin Ali (A.S.).
[5] Amirul Muminin (A.S.) ya ce "ku tsarkaku da ruwa daga mummunan wari kuma ku sabar wa kanku domin Allah yana fushi da bayinsa kazamai wadanda ke gundurar wadanda suka zauna tare da su." Tuhaful Ukul shafi na 24.
[6] Abin nufi da zikirin Allah ba wai shi ne ka yi ta maimaita kabbara da tasbihi da makamantansu ba kawai sai dai adinda ake nufi shi ne kamar yadda Imam Sadik (A.S.) ya bayyana a tafsirin ayar zikirin Allah inda Ya ce: "Ni ba na cewa subhanallah walhamdulillah wa La ilaha illallah wallahu Akbar koda yake shi ma yana daga cikinsa amma Zikirin Allah shi ne a cikin kowane hali idan ka himmatu da da'a ko sabo."