Home Page
 Tarihin rayuwarsa
   Akidojin Shi'a
   Littafansa
   Fatawoyi
   Sakonni
   Darussa
   Littafan dansa
   Dakin karatu
   Hotuna


Affiliate Websites
Affiliate Websites

   E-Mail Listing:


 

Hukunce-Hukuncen Salla

Salla ita ce mafi mahimmancin daga cikin bautar Ubangiji    madaukakin sarki,sannan idan aka karbi sallar mutum zaá karbi sauran ibadojinsa,idan kumwa baá karbi salla ba to ba za a karbi sauran ibadojinsa ba.Haka nan ta bangaren tsabta yayin da mutum ya yi salla saura biyar a rana wato ya ya kan tsarakake jikin sau biyar kenan. Haka nan salla guda biyar a rana takan tsarkake zuciyar mutum daga zunubi.Sannan ya kamata mutum ya yi salla a farkon lokacin sallar,saboda haka wanda yake wulakanta salla ko ba ya ba ta muhummanci kamar wanda ba ya yin salla ne.Manzo mai tsira yana cewa:"Duk wanda ba ya ba salla muhimmanci wannan mutumin ya canci azabar lahira." Wata ran manzo s.a.w.a yana zaune a cikin masallaci sai wani mtum ya shigo masallaci ya cigaba da salla,sannan ya kanyi rukuú da sujada  ba kamar yadda ya ya kamata ba,sai manzo ya ce:"Idan wancen mutum ya mutu a wannan halin da yake bai mutu ba kana addinina".Saboda haka ya kamata mutum ya hankali ta yadda ba duk yadda ya ga dama ba ne zai gabatar da salla, ya kamata mutum ya yi kokari ya gabatar da salla kamar yadda ya kamata.wato ya kasance yana salla tare da tunanin Allah madaukaki kuma kamar yadda Allah ya umurta a yi sallar.Wato mutum ya fahimci da wa ya ke ganawa,Sannan ya san cewa yana gaban wanda yake shi ne Allah mai girma da daukaka wanda komi yake a hannunsa.Saboda haka idan mutum ya kasance kamar haka yayin salla,Mutum zai manta da kansa ba wani abu da yake tunani sai Allah Madaukai,Kamar yadda aka cire kibiya daga jikin Imama Ali a.s. yayin da yake salla ba tare da ya sanya abin da ake yi ba.

Haka nan dole ne mai salla ya rik a tuba ga Allah  wato ya kaurace wa dukkan abin da zai hana karbar sallarsa,kamar hassada yi da mutane karya da makamantansu.haka nan mutu ya lizimci yin sauran abubuwan da Allah madaukaki ya wajab a kansa kamar bayar da zakka da khumusi da makamantansu.Wato a takaice mai salla dole ne ya kauce wa duk abin yake Allah madaukaki ba ya si bayinsa su aikata shi, sannan ya riki dukkan abin da Allah ya hori bayinsa da su rika aikatawa.Sannan mutu ya kaurace wa dukan abin da suke rage ladar salla wato kasan ce cikin tsabata,haka nan mutum ya kaurace wa kallon sama yayin da yake cikin salla.haka nana mutum ya riki abubuwan da suke kara ladar salla, kamar sanya zoben Akik da sanya tufafi masu tsabta da sanya turare, haka nan mutum ya lizimci tsabtace bakinsa da dai makamantansu.