Home Page
 Tarihin rayuwarsa
   Akidojin Shi'a
   Littafansa
   Fatawoyi
   Sakonni
   Darussa
   Littafan dansa
   Dakin karatu
   Hotuna


Affiliate Websites
Affiliate Websites

   E-Mail Listing:


 

Sallar Gufaila:

Mas'ala ta 774: daya daga cikin sallolin mustahabbi ita ce sallar Gufaila,wannan sallae kuwa a na yinta tsakanin sallar magarib da Isha,Lokacin wannan salla si ne bayan gama sallar Magrib har ya zuwa lokacin da jan rana na yamma zai bace,sannan wannan salla raka'a biyu ce,a raka'a ta farko bayan karanta fatiha ana karanta wannan aya maimakon sura, kamar haka:

«وَذَاالنُّونِ اِذْ ذَهَبَ مُغاضِباً فَظَنَّ اَنْ لَنْ نَقْدِرَ عَلَيْهِ فَنَادَى فِى الظُّلُماتِ اَنْ لا اِلهَ اِلاّ اَنْتَ سُبْحانَكَ اِنّى كُنتُ مِنَ الظّالِمينَ فَاسْتَجَبْنا لَهُ وَنَجَّيْناهُ مِنَ الغَمِّوَكَذلِكَ نُنْجِى الْمُؤمِنينَ».

A raka ta biyu kuwa bayan an karanta fatiha ana karanta wannan aya maiamakon sura kama haka:

«وَعِنْدَهُ مَفاتِحُ الْغَيْبِ لا يَعلَمُها اِلاّ هُوَ وَيَعْلَمُ ما فِى البَرِّ وَالْبَحْرِ وَما تَسْقُطُ مِنْ وَرَقة اِلاّ يَعْلَمُها وَلا حَبَّة فىِ ظُلُماتِ الاَرْضِ وَلا رَطْب وَلا يابس اِلاّ فِي كتاب مُبين».

Sannan ana karanata wannan addu'ar a yayin Kunut kamar haka:

 «اَللّهُمَّ اِنّى اَسأَلُكَ بِمَفاتِحِ الغَيْبِ الَّتى لا يَعْلَمُها اِلاّ اَنْتَ اَنْ تُصَلِىّ عَلى مُحَمَّد وَآلِ مُحَمَّد وَاَنْ تَفْعَلَ بى كذا وكذا.....

Sai mutum ya fadi bukatarsa idan ya isa wajen da da sanya kaza wa kaza.

«اَللّهُمَّ اَنْتَ وَلِىُّ نِعْمَتى وَالْقادِرُ عَلى طَلِبَتى تَعْلَمُ حاجَتى فَأساَلُكَ بِحَقِّ مُحَمَّد وَآلِ مُحَمَّد عَلَيْهِ وَعَلَيْهِمُ السَّلامُ لَمَّا قَضَيْتَها لى».

Hukuncin alkibla:

Mas'ala ta 775:Dakin Ka'aba wanda yake a garin makka shi ne alkibala kuma wanda ake fukanta yayin da matum yake salla.Saboda haka wanda yake nesa da shi idan ya fuskanci wajensa ta yadda za'a iya cewa ya kallai wajen ka'aba ya wadatar.Haka nan sauran wasu ayyukan kamar yanka dabba, dole ne a kallai kiblar yayin aiwatar da shi.

Mas'ala ta 776:Mutum zai  yi sallar wajibi daga tsaye,dole ya fuskanci kibla ta yadda za a ce yana kallon alkiba,amma ba wajibimba ne guyawunsa da "yan yaztsunsa su zama suna kallon kiblar.

Mas'ala ta 777: Mutum da zai yi salla daga zaune sannan kuma ba zai iaya zama ba kamar yadda kowa yake zama,ta yadda idan zai zauna sai dai ya kafa kafafunsa  a kasa, anan dole ne ya kasance kirjinsa,fuskarsa da cikinsa suna kallon kibla yayin da yake yin salla.Saboda haka ba dole ba ne kwaurin kafarsa ya zama yana kallom kiblar.

Mas'ala ta 778: Mutumin da kuwa ba zai iya yin salla ba daga zaune,a nan sai ya kwanta bisa kafadar dama ta yadda fuskarsa zata kalli kibla yayin da yake salla.Idan kuwa hakan ba zai yiwu ba yana iya kwantar kafadarsa ta hagu ta yadda gabansa zai kalli kiblar,Idan kuwa hakanma ba zai yiwu ba sai ya kwanta rigingine ta yadda tafin kafarsa zai kalli kiblar.

Mas'ala ta 779:Idan mutum zai yi sallar ihtiyat ko ramuwar tahiya ko sujjada,dole ya zama yana kallon kibla,haka nana yayin sujjadar Sahawu.

Mas'ala ta 780:Idan mtutm yana bisa abin hawa kamar mota,jirgi ko jirgin ruwa, yana iya sallar mustahhabi a wannan lokacin ba tare da ya kalli kibla.

Mas'ala ta 781:Mutumin da yake so ya yi salla dole ne ya yi kokari ya gano kibla, idan mutum yana so ya samu tabbas akan hakan yana iya samu adalai guda biyu su tabbatar masa da hakan wato wadan da zasu ba da shaidar ne bisa la'akari da abin da suka lura da shi na cewa lallai nan ne kiblar, ko kuma ta hanayr mutumim da yake da ilimin hakan,wato masanin hakan ta hanyar ka'idar ilimi.Idan kuwa hakan ba ta samu ba,sai mutum ya yi mafani da abin yake zaton hakadin ne, ta hanyar masallatan musulmi ko makanartasu, ta yadda mutum zai samu natsuwa a kan hakan.koda kuwa ta hanyar Fasiki ko kafiri idan har sun amfani da ka'idar ilimi uska fadawa mutum cewa nan ne kibla kuma mutum yana ganin haka ne koda bai samu tabbas ba, wannan ya wadatar.

Mas'ala ta 782:Mutum da yake tsammanin kibla idan har yana iya samuntsammanin da yafi wannan karfi,anan ba zai yi mafani da wannan tsammanin nasa ba,misali idan bako ya samu tsammanin cewa nana= ne kibla ta hanyar fadar mai masaukinsa,idan yana wata hanyar da zai kara samun nastuwar da fi wanna kamar ta hanyar yin amafani da na'urar gane kibla,anan dole ne ya yi mafani da ita domin hakan,bai kamata ya dogara da maganar mai masaukinsa ba.

Mas'ala ta 783:Na'urar da ake amfani a su wajen gano kibla idan har lafiya lau suke suna daya daga cikin hanyar da ake bi wajen gane kibla,saboda haka dogara da abin da suka nuna yafi sauran hanyoyin da za a iya bi wajen gano kiblar.

Mas'ala ta 784:Idan mutum ba sai inda kibala take ba,yana gano hakan ta hanyar duba inda masallatai suke kallo ko kuma ta hanayr Makabartar musulmi,amma idan mutum ya gano kibla sabanin inda masallatai suke nunawa, misali idan yayi amfani da na'urar gano kibla,anan ihtiyat wajib shi ne yayi amfani da abin wannan na'urara ta nunamasa kda kuwa ya sabawa Masallatan.Amma idan mutum samu tsammanin cewa musulmi da suke zaune a wannan wuri ba su taka tsantsan ba wajen gano kibla yayin da suke gina mallatansuda makabartunsu ba,anan mutumyana iya yin salla fuskar da ya ga ya fi natsuwa akan cewa ita ce kibla.

Mas'ala ta 785:Idan ba shi hanyar da zai yi ya gano kibla ko kuma ya yi kokarin ya gano amma ya kasa bada karfi waje guda,a nan idan akwai lokacin sai ya yi sallar har sau hudu wato ya yi salla hudu  kowa ne bangare,amma idan ba shi da cikkaken lokacin da zai yi salla guda hudu anan sai ya yi wadn da suka sawaka,wato idan kawai salla daya zai iya yi kowane bangare sai ya yi dayan,ta yadda dai zamu tabbas a kan cewa cikin wadan nan sallolin tabbas ya yi wata daga ciki ta fuskar alkibla.

Mas'ala ta 786:Idan mutum ya samu tabbas a kan cewa lallai kibla tana daya daga cikin bangarorin biyu,a nan dole ne mutum ya kalli wadan bangarorin guda biyu ya yi sallar,ihtiyat mustahab kuwa shi ne ya kalli dukkan bangarorin guda hudu ya yi sallar.

Mas'ala ta 787:Mutum da ya wajaba ya yi salla ta bangarori  fiye da daya,idan yana so ya yi sallat Zuhr,Asr, Magri da Isha, Abin da ya fi shi ne ya yi sallar farko ta dukkan fuskokin da suka wajaba  ya yi sallar,sannan ya yi salla ta biyu da haka dai har ya gama.

Mas'ala ta 788:Mutum da ba shi tabbas a ka n kibla idan zai yi wani abiu wanda kallon alkibla ya wajaba,misali idan zai yakka wata dabba,anan sai ya yi yankan ta bangaren da yake zaton nan ne kiblar,idan kuwa babu wani bangare da yake tsammani a nan sai ya kalli duk bangaren da yake so ya inganta.

Mas'ala ta 789:Idan mutum yana zaton wani bangare nan ne kibla sai ya fara salla,yana cikin salla sai kuma zatonsa a kan kibala ya koma zuwa ga wani bangaren,a nan dole ne ya juya ya ida sallar ga wannan bangaren na biyu da yake tsammani nan ne kibla.Amma idan ya zamana raka'o'in da ya riga ya yi sun kasance bayan kibla ta biyu da yake tsammani ne, ko kuma dama ko hagunta, a nan ihtiyat wajib shi ne ya sake wannan sallar zuwa kiblar da yake tsammani ta biyu.

Mas'ala ta 790:Idqan mutum ba tare da kula ba ya fara salla,sai bayan ya gama salla sai ya fahimci cewa ya yi sallar ne yana kalloon kibla,sannan ya yi sallarsa ne tare niyyar kusanci zuwa ga Ubangiji, a nan sallarsa ta inganta.Amma idan bayan ya gama salla sai ya fahimci cewa wajen da ya yi salla ba kibla ba ce,a nan sallar ta baci kuma dole ya sake ta wajen da kibla take.Amma a nan Alkibla ana ba wai sai dari bisa dari mutum ya kalli saitin Ka'aba ba, idan mutum ya kalli wajen da take koda ya dan kauce kadan babu laifi.

Mas'ala ta 791:Idan mutum ya yanka wata dabba sabanin kibla kuma da ganganci naman wannan dabbar ya haramta,amma idan mutum bai san inda kibla take ba ko kuma ya manta ko kuma sakamakon wani uziri bai san kiblar ba, idan ya yanka wata dabba a nan ya halatta a ci namanta.